Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta bayyana cewa zata tabbatar da sake jaddada dokar da ta haramta ɗaukar fasinja a kan kowane irin babur, tare da takaita zirga-zirgar adaidaita sahu daga ƙarfe 10 na dare zuwa 6 na safe.
Dokar, wadda Gwamnatin Jihar Kano ta riga ta sanar da ita tun a baya, ta shafi wasu kananan hukumomi da suka haɗa da: Kano Municipal, Gwale, Dala, Fagge, Nassarawa, Tarauni, Kumbotso, Ungogo (yankin Jido) da Dawakin Kudu (Tambuwal, Gurjiya da Jido).
Hakan n kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikowa Kadaura24.
Rundunar ta ce an baiwa tawagar jami’an tsaro ikon kama wa da bincikar duk wanda ya karya wannan umarni, tare da magance yada bayanan bogi da ka iya tayar da hankalin jama’a.

Ta kuma nuna cewa matakan an ɗauke su ne domin ƙara tabbatar da tsaro a fadin jihar, sannan duk wanda aka samu yana keta dokar zai fuskanci hukunci.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya bukaci al’umma da su bi ka’idojin, tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargin ka iya tada hankalin al’umma ga ofishin ’yan sanda mafi kusa ko kuma ta layukan gaggawa na rundunar.
Ganduje ya mayarwa da gwamantin Kano martani
Rundunar ta ce zata yi aiki tare da hukumar KAROTA domin tabbatar da cikakken bin doka da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.