Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da adalci, aiyukan more rayuwa da kyakkyawan shugabanci, a yayin taron shekara-shekara da kungiyar CREED ta shirya a Tropical Galeria, Kano.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Gwamnan, wanda Babban Lauya kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Barista Abdulkarim Kabiru Maude, SAN, ya wakilta, ya yaba wa masu shirya taron bisa yadda suke ƙarfafa tattaunawa mai ma’ana kan tabbatar da doka, jagoranci da cigaban al’umma.
A jawabinsa, Gwamnan ya jaddada irin gyare-gyaren ta ɓangaren shari’a da gwamnatinsa ke aiwatarwa, musamman batun sake duba tsare-tsaren da suka daɗe a cibiyoyin gyaran hali, wanda ya bankaɗo matsalolin da suka haɗa da mutane da aka tsare na tsawon shekaru ba tare da shari’a, ko takardun shari’a ba, ko kuma ba tare da lauya ba.
Ya bayyana cewa an ɗauki matakan gaggawa don nemo takardun shari’a da suka ɓace, fitar da shawarwarin shari’a, tare da sakin wadanda bincike ya nuna ya kamata a sake su.