Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan Nigeria ‘Yan Aji na 33 a kwalejin horon soja ta National Defence College (NDC) a ranar Alhamis.

Da yake jawabi bayan karɓar rahoton, Tinubu ya ci alwashin yin nazari kan shawarwarin da suka bayar game da yadda za a shawo kan matsalar tsaron ƙasar.

“Dole ne mu ci gaba da gina Najeriya, kuma haƙƙinmu ne samar da mafita daga shawarwarin da kuka bayar,” in ji shi.

InShot 20250309 102512486

Shawarwarin nasu na zuwa ne daidai lokacin da ake fargaba da kuma tafka muhawara game da barazanar Shugaban Amurka Donald Trump ta kutsawa Najeriya domin kare Kiristocin ƙasar bisa iƙirarin da ya yi – ba tare da hujja ba – cewa ana yi musu kisan gilla.

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Kwamandan kwalejin, Rear Admiral Abdullahi Ahmed, ya ce Aji na 33 ya ƙunshi ɗalibai 99, ciki har da jami’ai 25 na sojan ƙasa, 16 daga sojan ruwa, 12 daga sojan sama, biyar daga rundunar ‘yansanda, 18 daga ma’aikatun gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...

Matasan Arewa 10 sun shiga jerin karɓar lambar yabo ta shugabanci ta Afirka

Hankula sun koma zuwa ga Arewa yayin da matasa...