Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin Manjo-Janar Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) a matsayinsa na shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) na wasu shekaru biyar.

Marwa, wanda aka fara nada wa mukamin a watan Janairun 2021 a zamanin Shugaba Muhammadu Buhari, ya yi shekaru biyu a matsayin shugaban kwamitin ganin bayan ta’ammali da miyagun kwayoyi kafin a nada shi kan mukamin NDLEA.

Hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasa Bayo Onanuga ya rabawa manema labarai a yau juma’a .

InShot 20250309 102512486

Sake nadin na nufin tsohon hafsan soja ɗan asalin jihar Adamawa zai ci gaba da jagorantar hukumar har zuwa shekarar 2031.

Buba Marwa, wanda ya taɓa zama gwamnan soja na jihohin Legas da Borno, ya yi karatu a Makarantar Soja ta Najeriya da kuma NDA.

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Gabanin nadinsa, hukumar ta yi fice wajen gano miyagun kwayoyi, ciki har da cafke fiye da mutum 73,000 da ake zargi da safarar kwayoyi, da kama sama da tan miliyan 15 na miyagun kwayoyi daban-daban.

Haka kuma hukumar ta kaddamar da yunkurin wayar da kan al’umma kan illar shan miyagun kwayoyi a fadin kasar.

A cewar Shugaba Tinubu:
“Wannan sake nadin hujja ce ta gamsuwa da kokarin da ka yi na dakile safarar miyagun kwayoyi da kuma yaduwar su. Ina kira a gareka da cewa kada ka sassauta, musamman wajen bibiyar masu safarar kwayoyi da ke barazana ga rayuwar matasanmu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...

Matasan Arewa 10 sun shiga jerin karɓar lambar yabo ta shugabanci ta Afirka

Hankula sun koma zuwa ga Arewa yayin da matasa...