Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Date:

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji a jihar Kano, ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC a hukumance tare da abokinsa ɗan majalisar wakilai Rt. Hon. Sagir Koki, mai wakiltar Birnin Kano da kewaye.

A cewar Jibrin Kofa, an karɓe su hannu biyu-biyu a zauren majalisar wakilai daga manyan jami’an gwamnati da jam’iyyar APC. A wajen tarbar akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin; Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila; Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda; tsohon Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje; da kuma wasu fitattun jagororin jam’iyyar daga Kano da fadin ƙasar.

InShot 20250309 102512486

Jibrin ya bayyana godiya ta musamman ga Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, da sauran ‘yan majalisa da sanatoci bisa kyakkyawar tarbar da suka yi musu. Ya ce za su ci gaba da aiki tare da sauran ‘yan jam’iyyar domin ci gaban ƙasa cikin jajircewa da sadaukarwa.

Idan za a iya tunawa Dan majalisar tun a ranar laraba ya tara magoya bayansa na kananan hukumomin kiru da Bebeji domin neman shawararsu kuma suka Amince a koma APC , wanda Kofa ya tabbatar da hakan a zauren majalisar wakilai ta Kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Matasan Arewa 10 sun shiga jerin karɓar lambar yabo ta shugabanci ta Afirka

Hankula sun koma zuwa ga Arewa yayin da matasa...