Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a kan kudirin dokar kafa Gaya Polytechnic, mataki da ya nuna jajircewar gwamnatinsa wajen faɗaɗa damar karatun gaba da sakandare mai inganci a fadin jihar.

Wannan na cikin sanarwar da mai magana da yawun Gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya aikowa Kadaura24 a ranar Juma’a.

Yace An gudanar da bikin sanya hannu a Fadar Gwamnatin Kano, inda Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Rt. Hon. Jibril Ismail Falgore, da Mataimakinsa, Rt. Hon. Muhammad Bello Butubutu, suka harta.

InShot 20250309 102512486

A yayin taron, Gwamna Abba, ya nuna farin cikinsa bisa yadda aka gudanar da dukkan matakan majalisa cikin kwanciyar hankali, tare da yabawa shugabancin majalisar bisa himmarsu wajen gina tsari mai ɗorewa ga bangaren ilimi a jihar.

Gwamnan ya ce kafa Gaya Polytechnic zai ba da sabbin damammaki ga matasa don koyon sana’o’i da fasahohin da za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki.

Ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na farfaɗo da ilimi, ƙarfafa shi da kuma faɗaɗa damar koyo a matakai daban-daban, yana mai cewa sabuwar Makarantar fasahar muhimmiyar dama ce da za ta inganta rayuwar matasan jihar Kano.

Sanarwar ta ce kafa Gaya Polytechnic ya yi daidai da shirin gwamnatin jihar na samar da ilimi mai sauƙin samu ga kowane yanki, tare da ƙarfafa tattalin arzikin kananan hukumomi a sassan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...

Matasan Arewa 10 sun shiga jerin karɓar lambar yabo ta shugabanci ta Afirka

Hankula sun koma zuwa ga Arewa yayin da matasa...