Matasan Arewa 10 sun shiga jerin karɓar lambar yabo ta shugabanci ta Afirka

Date:

Hankula sun koma zuwa ga Arewa yayin da matasa goma daga Arewacin Najeriya da suke shugabanci a harkokin kasuwanci suka samu gurbin karɓar lambar yabo ta CEO’s Network Africa Awards 2025, wacce ke yaba wa hazikan masu kirkira da shugabanni da masu kawo sauyi a nahiyar Afirka.

Za a gudanar da bikin bayar da lambar yabon a ranar 14 ga Disamba, 2025, a Harabar Majalisar Tarayya, Abuja, inda za a karrama mutune 140 daga cikin masu takara sama da 15,000 da aka gabatar daga sassan nahiyar – adadi mafi girma tun kafuwar shirin.

Daga cikin wadanda suka fito daga Arewa a bana akwai hadakar ’yan kasuwa da ’yan wasa da masu fasaha da masu fafutukar tallafawa al’umma da ke sake fasalta ma’anar jagoranci a Afirka ta zamani.

InShot 20250309 102512486

A rukuni na “Ɗan Kasuwa na Shekara”, sun hada da Aliyu Mohammed, Shugaban Kamfanin Sarkin Mota Cars; Al-Amin Muhammed Idris, Shugaban Interface Africa; da Fatima Babakura, wanda ta kafa Yerwa Secrets da Timabee. Waɗannan sunaye sun shahara wajen kirkire-kirkire da ci gaban kasuwanci da matasa ke jagoranta.

A rukuni na “Noma”, Aminu Nyako, Shugaban Sebore Group, yana wakiltar bangaren kasuwancin noma, inda yake fafutukar ganin an cimma isasshen abinci da ci gaba mai ɗorewa.

A “Waka da Nishaɗi”, fitaccen mawaki Joseph Justice Elsa, wanda aka fi sani da Firstklaz, yana ɗauke da tutar Arewa yayin da tasirinsa ke ƙaruwa a duniyar wakoki.

A bangaren “Siyasa da Gwamnati”, Sadiq Rabiu, Mataimaki ga Shugaban Ƙasa na Musamman kan Ci gaban Ƙwarewa, ya samu gurbi saboda gudunmawarsa wajen inganta matasa da sabbin dabarun manufofi.

A “Tasirin Jama’a”, matasa mata masu ƙwazo kamar Hassana Maina, Daraktar ASVIOL Support Initiative; da Asma’u Ribadu, Jami’ar Tasiri ta Yola Hub, suna samun yabo saboda aikin su wajen kawo canji da haɗa kan al’umma.

A “Wasanni da Lafiya”, Shawall Barau, Shugaban ƙungiyar kwallon kafa ta Barau FC, ya fito a fili saboda jagorancinsa wajen amfani da wasanni a matsayin hanya ta ƙarfafa matasa da ci gaban al’umma a fadin Najeriya.

Tare da taken “Driving Africa’s Resilient Reinvention” (Tukumar Sabon Ginshikin Dorewar Afirka), wannan kyauta ta 2025 na nufin haskaka sabon ƙarni na masu hangen nesa a nahiyar. Yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen babban taron, idanu na mayar da hankali kan wadannan fitattun matasa goma daga Arewa – kuma tambayar da kowa ke yi ita ce: waye zai lashe kambin bana?

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...