Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Date:

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir Ibrahim Koki, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP.

A cikin wata wasikar da ya aikawa shugabar jam’iyyar ta mazabar Zaitawa , mai dauke da kwanan watan 11 ga Nuwamba, 2025, Sagir Koki ya ce ya yanke wannan shawara ne saboda rikicin cikin gida da ya dabaibaye jagorancin jam’iyyar a matakin ƙasa.

InShot 20250309 102512486

“Wannan rikici ya sanya da wuya in ci gaba da gudanar da aikina yadda ya kamata wajen wakiltar jama’ata na Kano Municipal a majalisar wakilai.” Inji Koki

Dan majalisar ya bayyana godiyarsa ga jam’iyyar NNPP bisa damar da ta ba shi ya wakilci jama’a a karkashinta, yana mai cewa gogewar da ya samu da kuma goyon bayan da aka nuna masa “sun kasance abin alfahari a gare shi hakan tasa dole ya gode mata.”

Ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da girmama shugabannin da mambobin jam’iyyar a kowane mataki.

Wasikar ta fara aiki daga ranar Talata, 11 ga Nuwamba, 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...