Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Date:

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya bayyana cewa ya fara harkokin siyasa tun kafin tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya fara taka rawa a manyan mukaman gwamnati.

Barau, wanda aka dade ana damawa da shi a siyasar Kano, ya ce ya shafe shekaru yana gudanar da ayyukan jam’iyya da fafutukar siyasa, a lokacin da Kwankwaso ke aiki a ma’aikatar ruwan sha ta jihar Kano. A cewarsa, hakan na nuna cewa ya riga tsohon gwamnan shiga fagen siyasa da dogon lokaci.

InShot 20250309 102512486

Sanata Barau ya bayyana haka ne yayin da yake karin haske kan tafiyar sa ta siyasa tun daga matakin matashi har zuwa matsayin da yake rike da shi a yau a majalisar dokoki ta tarayya.

Barau ya ce gogewar da ya tara tsawon shekaru ta taimaka masa wajen fahimtar yadda siyasa ke tafiya a Kano, musamman yadda dabi’u da tasirin ’yan siyasa ke sauyawa lokaci zuwa lokaci.

Masu sharhi kan siyasa sun ce furucin Barau na iya zama wani bangare na kokarinsa na fayyace irin rawar da ya taka a siyasar Kano tun kafin wasu fitattun sunaye su fara hawa manyan mukamai, tare da tunasar da irin yadda tarihi ya gina siyasar jihar zuwa matsayinta na yau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...