Fadar shugaban kasa ta yaba wa Kwankwaso bisa martanin da ya yi wa Trump kan barazana ga Najeriya

Date:

Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yaba wa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bisa sukar da ya yi wa Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, saboda maganganun sa masu tayar da kura da ke barazanar yiwuwar kai harin soji a Najeriya.

Mai magana da yawun fadar shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya bayyana matsayar Kwankwaso a matsayin ta kishin ƙasa, yana kira ga sauran shugabannin jam’iyyun adawa su bar siyasa a gefe, su tsaya tsayin daka wajen kare martabar ƙasar nan a gaban abin da ya kira “ɗaukacin ƙalubalen waje.”

FB IMG 1753738820016
Talla

“Mun gode Sanata Kwankwaso saboda kishin ƙasa. Wannan lokaci ne da ya dace dukkan shugabannin siyasa, ba tare da la’akari da jam’iyya ba, su haɗa kai su tsaya wajen kare ƙasarmu a matsayin ‘yan ƙasa na gari,” in ji Onanuga.

Kwankwaso ya yi tsokaci kan barazanar da Trump ya yiwa Nigeria

Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a karkashin jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, ya fitar da wata sanarwa inda ya yi gargaɗin cewa maganganun Trump na iya tayar da husuma ta addini da kuma ƙara ta’azzarar matsalar tsaro a ƙasar.

A shafinsa na X , tsohon gwamnan ya yi Allah wadai da matakin Trump na sake kiran Najeriya “ƙasa mai damuwa ta musamman” bisa zargin “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...