Kwankwaso ya yi tsokaci kan barazanar da Trump ya yiwa Nigeria

Date:

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya buƙaci Amurka ta taimakawa Nijeriya wajen yaƙi da ta’addanci maimakon barazana.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar yau Lahadi.

FB IMG 1753738820016
Talla

Kwankwaso yace “Na lura da yadda Shugaba Donald Trump ya nuna damuwa kan Najeriya. Yana da mahimmanci na jaddada cewa ƙasarmu ƙasa ce mai ‘yancin kai wadda mutanenta ke fuskantar barazana daban-daban. Rashin tsaron da muke fuskanta ba shi da alaƙa da addini, ƙabila, ko siyasa.”

Donald Trump ya yi barazanar daukar matakin soji a kan Nigeria

“Ya kamata Amurka ta taimaki hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance waɗannan matsalolin, maimakon yin barazana da za ta iya ƙara raba ƙasarmu.”

Kwankwaso yace ya kamata gwamnatin Najeriya ta naɗa wakilai na musamman daga manyan jami’an diflomasiyyarta don shiga tsakani da gwamnatin Amurka.

Ya jaddada cewa ya zama dole a naɗa jakadu don wakiltar muradun Najeriya a fagen ƙasa da ƙasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...