Donald Trump ya yi barazanar daukar matakin soji a kan Nigeria

Date:

Shugaban Kasar Amuruka Donald Trump ya yi barazanar daukar matakin soji a Najeriya, yana mai zargin gwamnatin kasar da kyalewa ana kashe kiristoci.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji don kakkaɓe abin da ya kira ƴanta’adda masu kishin Islama da ke aikata ta’asa.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ya kuma yi barazanar dakatar da duk wani taimakon Amurka ga Najeriya.

Tuni Najeriya ta yi watsi da ikirarin cewa ana kashe kiristoci ba gaira ba dalili a yankin arewacin inda galibi musulmi suka fi yawa.

A bayanin da Mista Trump ya wallafa a kafar sadar zumuntarsa ta Truth a ranar Asabar ya ce ya ba ma’aikatar tsaron Amurka ta fara shirin ɗaukar mataki kan Najeriya – “Idan har gwamnatin Najeriya ta bari ana ci gaba da kashe musulmi,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...