Ra’ayi: Shin ko da gaske ne an dakatar da shugaban karamar hukumar Bebeji dake Kano ?

Date:

Ra’ayin Isah Suleiman Ismail
31 Oktoba, 2025

A Yau juma’a, an soma yaɗa labarai cewa wai majalisar kansilolin Karamar Hukumar Bebeji ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar, Dr. Alhassan Salisu Bebeji. Wannan batu ya sa an tayar da jijiyoyin wuya, amma tambayar da ya kamata mu fara yi ita ce: A ina wannan dakatarwa ta samo asali ?

Gaskiya ita ce, doka ta bai wa kansiloli damar rubuta takardar neman a binciki ko a dauki mataki kan shugaban karamar hukuma, amma ba su da ikon su dakatar da shi kai tsaye. Dole ne su tura korafinsu zuwa majalisar dokoki ta jiha wacce ke da hurumin bincike da tabbatar da gaskiyar zargi, kafin a yanke hukunci.

Tambayar ita ce: Shin majalisar dokokin jihar kano ta karɓi korafin? Ta gudanar da bincike? Ta kira wanda ake zargi?.

FB IMG 1753738820016
Talla

Amsar ita ce: A’a. Saboda haka, ina kansilolin su ka samo ikon ayyana cewa wai sun dakatar da shugaban karamar hukumar ? Ya kamata su sani Doka ba ta ba su wannan hurumin ba.

Haka zalika, zaman da suka kira suna cewa tashinsa su ka yi a zauren majalisa, shin an yi shi ne bisa ka’ida? Shin akwai DPM ko CPO a wurin kamar yadda tsarin gudanar da zaman majalisa ke bukata?.

Amsar ita ma a’a ce. Ba a gudanar da wani zaman doka ba, kuma babu wani ma’aikacin gwamnati da ya tabbatar da hakan. Wannan ya sa al’amarin ya fi kama da taron gefen titi ko teburin mai shayi fiye da zaman majalisar doka.

Rikici a Bebeji: Jigon Kwankwasiyya na zargin an shirya cire sunayen tsoffin kansiloli domin yin kashe-muraba

Saboda haka, abin da kansilolin su ka yi ba wani abu ba ne illa katsalandan cikin hurumin da ba na su ba, kuma hakan na iya jawo musu matsala, domin majalisar dokokin jiha ba zata yi shiru a rika wuce gona da iri ba.

A tarihi ma, mutanen Bebeji ya kamata su tuna da irin wannan rikici da aka yi a zamanin Hon. Mudan Umar, lokacin da kansiloli 12 (banda na Gwarmai da Tariwa) su ka yi yunƙurin tsige shi amma abin yaci tura.

Haka ma a zamanin Ali Namadi, kansiloli 13 (banda na Gargai) su ka ayyana tsige shi amma abin ya ci tura, har ma aka dakatar musu da albashi saboda karya doka.

Saboda haka, wannan sabon rikicin ma bai sha bamban ba. Labarin dakatar da shugaban Bebeji tamkar wasan kwaikwayo ne kawai, ba wani abu da doka ta amince da shi ba.

Ku huta lafiya.

Wannan rubutun ra’ayin :

Isah Suleiman Ismail
31st October, 2025

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...