Yadda ƴansanda suka kama wasu da suke zargin ƴanbindiga ne a Kano

Date:

Rundunar yansanda ta Kasa reshen jihar Kano ta ce ta yi nasarar kama wasu da take zargin yanbindiga ne masu satar mutane domin kudin fansa.

Rundunar yansandan ta ce ta kama mutum biyu a ranar Asabar a yankin Shanono bayan samun bayanan sirri.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa Jami’in hulda da jama’a na rundunar yansandan jihar Kano ya shaida wa BBC cewa yanbindigar sun shigo ne daga jihar Katsina da ke makwabtaka da Kano.

Wannan na zuwa bayan mazauna yankin ƙaramar hukumar Shanono a jihar Kano sun koka game da yadda ‘yanbindiga masu satar mutane suka fara addabarsu suna satar mutane da kuma dabbobi.

SP Kiyawa ya tabbatar da cewa an samu kutsen wasu da ake zargin ƴanbindiga ne a yankin ƙaramar hukumar Shanono kuma suna satar mutane da dabbobinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...