Gasar Firimiya ta Ƙasa: Barau FC ta doke Kano Pillars 2-1 a Kano

Date:

A wani yanayi na al’ajabi, Kungiyar Kwallon Kafa ta Barau FC ta doke abokiyar burmin ta, Kano Pillars 2-1 a wasan mako na 9 na Gasar Firimiya ta Ƙasa (NPFL).

Barau FC ta bada mamaki ne bayan da ta farke kwallon da Pillars ta jefa mata sannan ta ƙara a wasan hamayya na farko a tarihi tsakanin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafan biyu da ke gari ɗaya.

Tun a minti na 20 da take wasan Rabi’u Ali ya ci wa Kano Pillars, Amma a minti na 52, Abdulbari Nura ya farke, inda daga bisani Stanley Oganbor ya ƙara, lamarin da ya jefa yan wasan kungiyar cikin murna da farin ciki.

Da ya ke tsokaci kan wasan, Shugaban kungiyar Barau FC, Shawall Barau Jibrin ya ce nasarar ta nuna irin ƙwazon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin wajen kafa ƙungiyar ƙwallon ƙafa da za a gafarta da ita a fadin ƙasar.

Ya ce nasarar ta nuna cewa lallai Barau FC za ta iya karawa a ko wanne matakin kwallon a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...