Dalilin da yasa gwamnan kano ya nemi Tinubu ya cire Kwamishinan yan sanda na jihar

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi kira ga shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu da ta gaggauta sauya kwamishinan ‘yan sanda na jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai.

Ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yadda kwamishinan ya janye jami’an tsaro daga filin wasa na Sani Abacha lokacin taron.

Ya ce wannan mataki bai dace ba, kuma ka iya barazana ga tsaro da zaman lafiya a lokacin da ake gudanar da muhimmin bikin a kasa.

Idan za a iya tunawa dangantaka tsakanin gwamnatin Kano da Rundunar Yan sanda ta Kasa reshen jihar Kano ta yi tsami sakamakon zargin da gwamnan ya yi na cewa yan sandan ba sa bin umarninsa tun daga lokacin da ya Zama gwamna a shekarar 2023

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...