Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Date:

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince da Naira miliyan 8.2 a matsayin kuɗin aikin Hajjin shekarar 2026.

Daraktan Hukumar, Lamin Danbappa, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Sulaiman Dederi, ya fitar a Kano.

Danbappa ya bayyana cewa kuɗin sun yi daidai da umarnin Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) kuma sun shafi dukkan masu niyyar zuwa aikin hajji.

Ya ce masu niyyar zuwa aikin hajji da suka riga suka ajiye Naira miliyan 8.5 za a mayar musu da ragowar kuɗin bayan sun rubuta takardar neman a maida musu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa, masu niyyar zuwa aikin hajji da za su fara biyan kuɗi yanzu ana sa ran su biya Naira miliyan 8.2 bisa ga umarnin da aka amince da shi.

Danbappa ya ƙara da cewa, ranar ƙarshe ta biyan kuɗin ita ce 31 ga Disamba, 2025, inda ya shawarci masu niyyar zuwa aikin hajji da su kammala biyan kuɗaɗen kafin lokacin domin tabbatar da gurbin tafiyarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...