Zargin kalaman ɓatanci: Majalisar Shura ta Kano ta gaiyaci Malam Lawan Triumph

Date:

Majalisar shura ta jihar Kano ta gaiyaci Sheikh Lawan Abubakar Triumph bisa ƙorafe-ƙorafe da aka miƙa mata na zargin furta kalaman ɓatanci ga Ma’aiki Annabi Muhammad (SAW).

Haka zalika majalisar ta gaiyaci waɗanda suka mika ƙorafe-ƙorafen domin zama a ji ta bakin ki wanne ɓangare.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan zaman majalisar na farko tun da aka kafa ta, Sakataren majalisar kuma Kwamishinan Kasuwanci, Shehu Wada Sagagi ya tabbatar da cewa an mikawa majalisar ƙorafe-ƙorafe har guda 8 daga kungiyoyin addini da na al’umma.

Ya ce majalisar ta duba ƙorafe-ƙorafen kuma za ta gayyaci kowanne ɓangare, har da shi ma Malam Triumph din don jin ta bakin sa.

Haka zalika Sagagi ya kara da cewa Majalisar za ta yi aiki tsakani da Allah don baiwa gwamnati shawarar da ta dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...