Yansanda a Kano sun kama ɗan ‘sandan bogi da ke karɓar kuɗi a hannun mutane

Date:

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Kano ta kama wani mutum mai shekaru 33 da ake zargi da zama ɗan sandan bogi domin yaudarar jama’a da karɓar musu kuɗi.

An gano wanda ake zargin mai suna Nasiru Shitu, mazaunin unguwar Kofar Waika a Kano, inda aka cafke shi a ranar Lahadi, 21 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, cikin wani kayan da ake zargin na ƴansanda ne.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansanda na jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, inda ya ce an kama Shitu ne a Kofar Dawanau, wani yanki da aka sha samun rahoton damfara daga masu ikirarin cewa ‘yan sanda ne.

“Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ba ɗan sanda ba ne, kuma ba ɗan sa-kai na Constabulary ba ne, sai dai mai kwaikwayo da amfani da sunan ƴan sanda domin karɓar kuɗi daga hannun jama’a,” in ji Kiyawa.

‎Ban taba Nadamar Aiki da Ganduje ba – Abba Anwar

Ya ƙara da cewa za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu, yayin da ake ci gaba da gudanar da ƙarin bincike domin gano irin yawan laifuffukan da ya aikata da kuma yiwuwar samun abokan harkallarsa.

Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yi kira ga jama’a da ke da bayanai ko ƙorafe-ƙorafe game da wanda ake zargin, ko makamantansa, da su tuntubi rundunar ta lambar gaggawa: 07038188127.

Rundunar ta kuma tabbatar wa jama’a cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar, tare da jajircewa wajen tabbatar da cewa duk masu aikata laifukan damfara sun fuskanci hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...