Tinubu ba zai halarci taron Majalisar Dinkin Duniya ba

Date:

Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima ne zai jagoranci tawagar ƙasar zuwa taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) karo na 80 da za a yi a watan nan, a cewar fadar shugaban ƙasa.

Hakan na nufin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba zai je taron ba, kuma wannan ne karo na biyu a jere da Shettima ke jagorantar tawagar ta Najeriya zuwa taron.

Sai dai fadar ba ta faɗi takamaiman dalilin da ya sa Tinubu ba zai je taron ba, wanda shugabannin ƙasashen dunya ke halarta duk shekara a hedikwatar MDD da ke birnin New York na Amurka.

An Yanka ta Tashi Game da Digirin Girmamawar da aka Baiwa Rarara

Wata sanarwa daga ofishin mataimakin shugaban ta ce Shettima zai bi sawun takwarorinsa na ƙasashen duniya wajen tafka muhawara a zauren daga ranar Talata zuwa Lahadi 28 ga watan Satumba.

Amma sai a ranar Laraba Shettima “zai gabatar da jawabin Najeriya a tsakanin ƙarfe 3:00 zuwa 9:00 agogon New York”, in ji sanarwar.

FB IMG 1753738820016
Talla

“Bayan kammala taron UNGA, mataimakin shugaban zai wuce Frankfurt na ƙasar Jamus, inda zai gana da jami’an Bankin Deutche kafin ya dawo Najeriya.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...