An Yanka ta Tashi Game da Digirin Girmamawar da aka Baiwa Rarara

Date:

Jami’ar European-American ta fitar da sanarwa da ta ke barranta kan ta da digirin girmamawa da aka baiwa shahararren mawaki, Dauda Kahutu Rarara ba, inda ta ce ba da izinin ta kuma ba ta yarjewa kowa ya bada digiri ga mawaƙin ba.

A wani taro da aka shirya a otal din Nicon Luxury a Abuja a jiya Asabar, wanda gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya halarta tare da wasu manyan baki, an baiwa Rarara wannan digiri na girmamawa ta hannun wasu mutane da suka nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

Amma a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin ta na yanar gizo, muhukuntan jami’ar sun nisanta kan su da Rarara da kuma jami’an da suka nuna kansu a matsayin wakilan jami’ar.

“Jami’ar ba ta ba da izinin gudanar da wani bikin kammala karatu a wannan wuri a yau ba, kuma wannan taron an shirya shi ne ta hanyar damfara ba tare da sanin jami’ar ba ko amincewarta.

FB IMG 1753738820016
Talla

” Wadanda suka shirya wannan taron sun yaudari wasu mutane cewa su ne wakilan Jami’ar European-American, amma wannan ba gaskiya ba ne, kuma ba su da wani hurumin yin hakan ko karbar kudi a madadin jami’ar,” in ji sanarwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...