Gwamna Abba Kabir ya sake ɗaukar Malamai sama da 4,000 aiki a Kano

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ɗauki malamai 4,315 aiki daga cikin tsoffin malamai masu aikin sa kai na BESDA domin su zama cikakkun ma’aikatan din-din-din .

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya aikowa Kadaura24 ranar Alhamis.

Ya ce, Gwamna Yusuf ya mika takardun ɗaukar aiki ga sababbin malamai a filin wasa na Sani Abacha, inda ya shawarce su da su kasance masu kishin aiki, gaskiya, da kuma baiwa dalibansu tarbiyya ta gari.

Ya ce a baya gwamnatin sa ta ɗauki malamai 5,500 a shekarar 2023, sai a shekarar 2024 ya ɗauki Malamai 5,632, yanzu kuma ya dauki 4,000 a watan Mayu 2025, dukkansu daga cikin shirin koyarwa na sa kai na BESDA.

Gwamnan ya ce wannan tsari alama ce ta jajircewar gwamnatinsa wajen gyara harkar ilimi a jihar Kano.

Don ƙarfafa tsarin ilimi, Gwamnan ya sanar da ɗaukar karin malamai 2,616, da kaddamar da shirin daba lamunin ababen hawa na Naira miliyan 200, tare da amincewa da rabon babura 444 da kwamfutoci 300 domin inganta kula da makarantu.

FB IMG 1753738820016
Talla

Haka kuma, ya bayar da umarnin sake buɗe makarantar kwana ta Shehu Minjibir wacce za ta fara da ɗalibai 180, da ɗaukaka darajar wata makaranta a karamar hukumar Ungogo zuwa makarantar kwana, sannan ya amince da ɗaukar masu gadi 17,000 a makarantu a fadin jihar.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa gyare-gyaren ilimi da gwamnatin sa ke aiwatarwa sun fara haifar da ɗa mai ido, inda aka yi la’akari da nasarar da Ɗaliban Kano suka samu a sakamakon jarrabawar NECO ta 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...