Gwamnatin Kano na neman Karin runfunan zabe a jihar

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci a samar da karin rumfuman zabe a mazabun jihar Kano domin rage cunkoson da ake fuskanta a lokacin zabe.

Shugaban kwamitin wayar da kan al’umma kan muhimmancin mallakar katin zabe kuma kwamishinan yada labarai Comred Ibrahim Abdullahi Wayya ne ya bukaci hakan lokacin da kwamitin ya ziyarci shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa reshen jihar Kano Amb. Abdu Zango a ofishinsa.

FB IMG 1753738820016
Talla

Comred Waiya ya ce an samu karin sabbin gundumomi da unguwanni a jihar Kano wadanda su ke bukar a shigar da su cikin jadawalin hukumar, inda ya kuma bukaci a rage alkaluman rumfuman da ake samun cunkoso zuwa sabbin rumfunan zaben da za a kirkira.

Ya shaidawa shugaban hukumar cewa kwamitin zai yi duk mai yiwuwa don tabbatar da jihar Kano ta rike kambunta na jihar da tafi kowace jiha yawan al’umma a kasar nan.

Ya kara da cewa a shirye kwamitin yake ya yi aiki kafada-da-kafada da hukumar domin wayar da kan al’umma tare da taimaka musu ta kowace fuska.

A nasa bangaren shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa reshen jihar Kano Amb Abdu Zango ya ce akwai sama da katin zabe 360,000 da har yanzu masu su basu zo sun karba na a jihar Kano.

Don haka ya bukaci kwamitin da ya wayar da kan wadanda suka yi rijista su zo ofishin hukumar domin karbar katinsu.

A yayin ziyarar, shugaban kwamitin na tare da wakilai da sakatarorin kwamitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...