Ba a ga watan Maulidi a Nigeria ba – Sarkin Musulmi

Date:

Fadar Mai alfarmar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad abubakar na III ta aiyana ranar Litinin 25 ga watan Agusta ta zama 1 ga watan Rabi’ul Auwal 1447.

Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addinin Musulunci a Majalisar Sarkin Musulmin kuma Wazirin Sakkwato Farfesa Sambo Wali Junaid ya fitar da bayanin cewa ba a samu ganin jinjirin watan Safar ba a ranar Asabar a Najeriya.

FB IMG 1753738820016
Talla

“Kwamitin Ganin Wata na Ƙasa da na Harkokin Addini a Majalisar Sarkin Musulmi ba su samu bayanin fitar sabon watan Rabi’ul Auwal ba a ranar Asabar 29 ga watan Safar.

Zargin Almundahana: EFCC da ICPC Sun Gano Naira Biliyan 6.5 A Asusun Guda Cikin Manyan Hadiman Gwamnan Kano

“Don haka Lahadi 24 ga watan Agusta za ta zama 30 ga watan Safar 1447,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa Sarkin Musulmi ya aiyana Litinin a matsayin farkon watan Rabi’ul Auwal bayan amincewa da rahoton rashin ganin wata da aka bayar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...