2027: Jonathan zai tsaya takarar shugaban ƙasa don karawa da Tinubu

Date:

Tsohon shugaban ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan, ya amince da tsayawa takarar shugabancin ƙasa a 2027, in ji wani amintaccen na jikinsa da ke cikin jam’iyyar PDP.

Vanguard ta rawaito cewa na jikin ma Jonathan ya ce, an kai matakin karshe wajen shawo kan Jonathan da ya tsaya takara domin farfaɗo da tattalin arziki da rage wahalhalun jama’a.

FB IMG 1753738820016
Talla

Majiyar ta bayyana cewa shirin dawowar Jonathan yana samun goyon bayan manyan shugabanni da dattawan ƙasa waɗanda suka yarda cewa mulkinsa na baya ya kwantar da tarzoma kuma ya daidaita tattalin arziki.

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dasa bishiyu miliyan 5 a jihar

An bayyana cewa Jonathan ya gana da tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida (mai ritaya), da kuma wasu manyan ‘yan siyasa na Arewa da Kudancin ƙasar don neman goyon baya.

Jam’iyyar PDP dai na ƙoƙarin ba Jonathan tikitin takara kai tsaye, tare da wasu jiga-jiganta da suka je Gambia domin shawo kansa.

Jonathan, a halin yanzu, yana ganawa da masu ruwa da tsaki daga yankin Kudu maso Kudu.

Sai dai akwai ce-ce-ku-ce kan ko doka za ta bari Jonathan ya sake takara, kasancewar an rantsar da shi sau biyu.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Amma wasu lauyoyi da wana hukuncin kotu a 2022 sun bayyana cewa gyaran dokar kundin tsarin mulki da aka yi a 2018 ba zai shafi Jonathan ba tunda ya yi mulki kafin gyaran ya fara aiki.

Jam’iyyar PDP na ganin Jonathan zai iya ceto Najeriya daga halin da take ciki, tare da sauya tsarin siyasar ƙasar idan ya amince da takarar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...