Yadda Kwamishina a gwamnatin Kano ya tsayawa wani dilan ƙwaya aka bada belin sa a kotu

Date:

 

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya wa Suleiman Danwawu, ƙasurgumin dilan miyagun ƙwayoyi aka bada belin sa a kotu.

Kwamishinan ya kawo wa Danwawu ɗauki ne bayan da Mai Shari’a MS Shu’aibu, alƙalin da yai suna wajen tsauri a shari’a, ya sanya sharuɗɗan beli masu tsauri.

Bayan ya yanke hukuncin bada belin Wanda ake zargi a ranar 16 ga Yuli, DAILY NIGERIAN ta gano cewa alkalin ya umarci wanda ake zargi da gabatar da kwamishina mai-ci a Jihar Kano a matsayin wanda zai tsaya masa, tare da ajiye Naira miliyan biyar (₦5,000,000) a kotu.

InShot 20250309 102512486
Talla

Sai dai kuma abin da ake ganin da kamar wuya a samu kwamishina a gwamnatin Abba Kabir Yusuf da zai tsaya wa wanda ake zargin da laifin safarar miyagun ƙwayoyi, sai gashi Namadi ya bugi ƙirji ya rubuta takarda, yana bayyana kansa a matsayin Wanda sai tsaya wa Danwawu.

A wata takarda da ya rubuta a ranar 18 ga Yuli, 2025, kuma ya aikewa mataimakin babban rajistaran Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, Namadi ya nemi a amince ya tsaya wa Danwawu a bada belin sa.

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa, a ranar 21 ga Mayu, Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) ta shigar da ƙara akan Danwawu mai ɗauke da tuhume-tuhume guda takwas da suka shafi safarar ƙwayoyi a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Kano.

Bayan gurfanar da shi a gaban kotu a ranar 28 ga Mayu, an dage sauraron buƙatar belin sa zuwa ranar 16 ga Yuni, sannan aka ajiye wanda ake zargin a gidan yari.

Ga takardar da ya rubutawa Kotun da kuma sauran bayanai

FB IMG 1753434260675 FB IMG 1753434279797 FB IMG 1753434270761 FB IMG 1753434267667 FB IMG 1753434273828

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...