Yanzu-yanzu: Karin bayani game da shirye-shiryen Jana’izar Buhari

Date:

Gawar tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta baro birnin London, Birtaniya, da safiyar Yau Talata, zuwa garin Daura a Jihar Katsina, domin gudanar da jana’izar sa.

Jaridar PUNCH Online ta ruwaito cewa an dauko gawar tsohon shugaban kasar ne a jirgin saman Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ke jagorantar tawagar gwamnatin tarayya da shirye-shiryen dawo da gawar tsohon shugaban kasar zuwa gida.

InShot 20250309 102512486
Talla

A jiya Litinin, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai karɓi gawar tsohon shugaban kasar a Katsina kafin a kai ta Daura don binne wa.

Ministan Watsa Labarai da Tsare-Tsaren Ƙasa, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a birnin Abuja.

Yanzu haka kuma rahotannin da Jaridar Kadaura24 ta samu daga Garin Daura, na tabbatar da cewa tuni aka Fara haka kabarin tsohon shugaban gidan a wani yankin daga cikin gidansa.

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Wani ganau ya shaidawa majiyar Kadaura24 cewa bayan an Binne Muhammadu Buhari akwai kyakykyawan zaton za a katange kabarin nasa.

Yanzu haka dai jami’an tsaro sun yiwa gidan Buhari dake garin Daura a jihar Katsina kawanya, domin tabbatar da cewa an yi jana’izar ba tare da wata matsala ba.

Sai dai har yanzu gwamnantin jihar Katsina ba ta sana da a Inda za a gudanar da Sallar jana’izar Buhari ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...