Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai a gobe Talata ne za a yi jana’izar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari wanda ya rasu ranar Lahadi a birnin Landa.
Yayin da yake jawabi ga manema labarai a fadar gwamnatinsa , Radda ya ce ya yi magana da iyalan tsohon shugaban ƙasar da kuma makusanta da ke Landan dangane da shirye-shiryen ɗaukar gawar zuwa Najeriya.

”Daga tattaunawar da na yi da iyalansa da makusantansa da ke tare da gawar, sun bayayna mana cewa ana ci gaba da shirye-shiryen yadda za a ɗauko gawar zuwa Najeriya”, in ji Gwamnan.
Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta
”Bayannan da na samu shi ne sai gobe da rana misalin ƙarfe 12:00 gawar za ta ƙaraso, don haka za a guanar da jana’izar da misalin ƙarfe 2:00 na ranar gobe Talata”, in ji gwamnan na Katsina.