Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar Dikko Radda ta ayyana litinin 14 ga watan yuli, 2025, a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan jihar domin yin juyayin rasuwar tsohon shugaban Kasa Muhammad Buhari .
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Katsina Abdullahi Garba Farkari ya fitar .

Sanarwar ta ce Gwamnan Radda ya ba da hutun ne domin baiwa ma’aikatan jihar damar bin sahun sauran yan Nigeria wajen yin alhinin Buhari da kuma nema masa rahamar Allah Madaukakin Sarki.
Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria
Sanarwar ta ce a madadin al’ummar jihar Katsina Gwamnan Radda na Mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan Muhammadu Buhari tare da Addu’ar Allah ya gafarta masa zunubansa ya Sanya shi a aljanna.