Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Date:

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa da tutocin Najeriya a ko ina a fadin Najeriya domin nuna alhinin rasuwar tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban kasa Bayo Onanuga ya fitar a Abuja .

InShot 20250309 102512486
Talla

Ya ce Shugaba Tinubu ya kuma baiwa mataimakinsa Kashim Shettima Umarnin  da ya tafi birnin London domin Shirin dawo da gawar marigayi Buhari.

Sanarwar ta kara dacewa,tuni Bola Tinubu ya kira uwar gidan Buhari Aisha Buhari ta wayar tarho ya nuna kaduwarsa da mutuwar marigayin.

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Tinubu yavce Najeriya ta yi rashin jajirtaccen mutum kuma dan kishin kasa.

Buhari  rasu ne a yammacin Lahadi a London yana da shekaru 82 da haihuwa a duniya.

Ya rasu ya bar mace daya da ya ya guda 10 da jikoki da yan uwa.

Ya ya biyar ya same su ne da tsohuwar matarsa Hajiya Safinatu Yusuf,sai ya ya biyar da ya samesu da uwar gidansa ta yanzu Aisha Halilu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...