Gamayyar wasu kungiyoyi sun bukaci Kotun kolin Nigeria ta gaggauta yanke hukunci kan rikicin Masarautar kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gamayyar kungiyar masu fashin baki da da rajin kare Dimokaradiyya da tabbatar da shugabanci Nagari ta bukaci Kotun kolin Nigeria da ta gaggauta yanke hukunci kan dambarwar Masarautar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban Gamayyar kungiyoyin Com. Al-amin Albarrah da sakataren kungiyar Malam Saminu Habubakar suka sanyawa hannu kuma suka aikowa Kadaura24.

Sanarwar ta al’ummar jihar Kano sun damu matuka da yadda aka Sami jan kafa sama da shekara guda wajen yanke hukunci kan dambarwar wanene sahihin Sarkin Kano.

InShot 20250309 102512486
Talla

” Mu Gamayyar kungiyoyin masu fashin baki da kare Dimokaradiyya da tabbatar da shugabanci Nagari, mun damu matuka da yadda hadarin da ke tattare da rashin yanke hukunci, da kuma yadda wasu mara kishi suke kokarin yin amfani da hakan wajen kawo cikas a shari’ar, wanda hakan zai iya haifar da rashin zaman lafiya a jihar”.

Gwamnan Kano Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikatan Fadar gwamnati

Sanarwar ta kara da cewa ” Muna kira ga alkalan Kotun kolin Nigeria da ku yi amfani da damarku wajen kawo karshen turkaturkar Masarautar Kano, domin yin haka shi ne zai tabbatar da samuwar Masarautun gargajiya a Wannan tsarin na Dimokaradiyya.

Gamayyar Kungiyoyin sun bukaci al’ummar jihar Kano da su kau da duk wasu banbace-banbance su cigaba da zama da juna lafiya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...