Mu na Maraba da duk wata Adawar Siyasa mai tsafta da za ta kawowa kano cigaba – Waiya

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta ce tana maraba da duk wata adawar siyasa mai tsafta wadda za ta haska mata wasu ayyuka da za ta bijiro da su don ciyar da jihar gaba.

Kwamishinan Yada labarai da al’amuran cikin gida na jihar Kano Kwamred Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan lokacin da yake kaddamar da kwamatin Iyayen kungiyar Yan gwagwarmaya masu magana a gidajen Radio lakanin Gauta Club.

InShot 20250309 102512486
Talla

Kwamared Waiya ya kuma godewa gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa yadda yake kokari wajen hada kan yan Adawar jihar don yin siyasa ba da gababa da kuma kokarin ciyar da jihar Gaba.

Da yake jawabi shugaban kungiyar ta Gauta Club Alhaji Hamisu Dan Wawu Fagge yabawa kwamishinan yada labarai yayi bisa yadda yake tafiyar da aikinsa daga ciki hadda yadda aka tsaftace siyasar Baka a gidajen Radio, in da yace har makwaftan jihohi sun fara sha’awar su suna masu neman iznin kwaikwayon wannan tsari na Jihar kano.

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Yayin karbar rantsuwar sabbin dattawan na Kungiyar Gauta daga jamiyyu daban daban sunyi Alkawarin rike gaskiya da Amana, da kuma bin doka da kaidah.

Daga nan sai wasu daga cikin su suka godewa kwamishinan yada labaran bisa yadda yake kokari wajen tsaftace adawar siyasa a jihar Kano.

Mutane goma sha hudu aka rantsar a matsayin kwamatin dattawan kungiyar ta Gauta Club, Wanda suka hadar da Alhaji Bashir Adamu Gaya, Idris Danzago, Alhaji Isah Bello Jaa, Alhaji Ibrahim Dan Adandan, Alhaji Damina Ali Gwarzo, Alhaji Auwalu Maiturare Bichi, Kwamred Rabiu Bala, Muhammad Idris Matashin Dan Fansho, Sauran sun hadar da Dan Jummai Gwaska, Injiya Dayani Tarauni, Lawan Sofi Danmasanin Gaya, Hajiya Binta Sayyadi, da Hajiya Habiba Dandalla, Sai kuma Hon. Aminu Bichi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...