Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Al’umma da Malaman makaranta a unguwar Hotoron Arewa dake karamar hukumar Nasarawa sun koka bisa rashin kyawun hanya da magudanan ruwa da ya addabi yankin su musamman duba da shigowar damunar bana.

Mazauna yankin sun ce hakan na matukar barazana da hana ya’yan zuwa makaranta.

InShot 20250309 102512486
Talla

Umar Dauda daya ne daga cikin Mazauna Hotoron Arewa Unguwar Kwari ya ce suna fuskatar kalubale mai yawa idan akai Ruwa, inda ya ce tana kaiwa ga idan anyi Ruwa ya’yansu ba sa iya zuwa Makaranta.

“Mun jima muna kokawa bisa yadda hanyar mu ta lalace wanda mun yi iya kokarin mu wajan gyaran hanyoyi da magudanan ruwa Amma hakarmu bai cimma ruwaba”. Umar Dauda

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Ya ce har kudi-kudi suka hada a kungiyance domin gyaran magudanan ruwan, amma Sai da su ka gama gyaran mamakon ruwan Sama da aka Samu a shekaran jiya ya Maida masu aikin baya.

Umar Dauda a madadin al’ummar unguwarsu ya na kira ga gwamnatin jihar Kano ta Mai girma Abba Kabir yusuf da shugaban karamar hukumar ta Nasarawa da a kai masu dauki dan kada karatun yaran su ya sami matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...