Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ta bukaci al’ummar Musulmin Nigeria da su fara duban jinjirin watan almuharram na shekara ta 1447.

“Gobe Laraba 25 ga watan yuni 2025, ita ce daidai da 29 ga watan zulhijja na shekara ta 1446 don haka ita ce ranar da za a fara duban jinjirin watan almuharram na sabuwar shekarar musulunci”.

InShot 20250309 102512486
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin harkokin addinin musulunci na fadar Sarkin Musulmi Farfesa Sambo wali Junaidu ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Sanarwar duk wanda ya ga watan ya sanar da wani basarake mafi kusa da shi domin mika sanarwar ga fadar mai alfarma Sarkin Musulmi domin tantancewa.

Kadaura24 ta watan Almuharram dai shi ne wata na farko a kalandar addinin musulunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...