RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Date:

Kungiyar ma’aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar Kano ta mika sakonta na taya murna ga Abbas Ibrahim saboda Sabon mukamin Dan kwamitin Amintattu na kungiya Yan Jarida ta Kasa NUJ .

” Babu shakka kungiyar NUJ ta kasa ta ajiye kwarya a gurbinta , saboda Muna da yakinin Abbas Ibrahim zai iya wannan aikin da aka dora masa kuma Muna da tabbacin ba zai Baiwa mutanen Kano kunya ba”.

InShot 20250309 102512486
Talla

Shugaban kungiya RATTAWU na jihar Kano Com. Babangida Mamuda Biyansu ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Com. Babangida Biyamusu ya yabawa shugaban kungiyar NUJ na kasa bisa Wannan kyakykyawan tunanin da ya na baiwa Abbas Ibrahim Wannan mukamin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

” A madadin dukkanin ya’yan kungiyar RATTAWU ta jihar Kano Muna taya dan uwanmu murnar Wannan Sabon matsayin da ya Samu, Muna kuma fatan Allah ya bashir ikon sauke nauyin da aka dora masa”. Inji Shugaban kungiyar RATTAWU ta jihar Kano .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...