NUJ@70: Gwamnan Kano ya karbi lambar girmamawa daga yan jarida

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Ƙungiyar Ƴan Jarida ta Nigeria (NUJ) ta karrama Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da lambar yabo ta musamman bisa goyon bayan da yake bai wa aikin jarida.

‎Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma, Alhaji Muhammad Idris, ne ya miƙa lambar girmamawar.

InShot 20250309 102512486
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

‎An bayar da lambar karramawar ne yayin bikin cikar kungiyar shekaru 70 da kafuwarta a birnin Abuja, inda mataimakin gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya karɓa a madadin gwamnan.

‎Shugaban NUJ na ƙasa, Kwamared Alhassan Yahaya, ya ce an zaɓi Gwamna Abba ne saboda irin goyon bayan da yake bai wa kafafen yaɗa labarai da kuma jajircewarsa wajen cigaban ƙasa, kare ’yancin fadar albarkacin baki da inganta shugabanci na gari.

IMG 20250415 WA0003
Talla

‎A nasa jawabin, mataimakin gwamnan ya taya Gwamna Abba murna, yana mai cewa karramawar ta nuna yadda gwamnatin Kano ke mutunta aikin jarida da ma dimokuraɗiyya baki ɗaya.

‎Kwamared Gwarzo ya kuma bayyana cewa Jihar Kano za ta karɓi bakuncin taron Kungiyar NUJ na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...