Iftila’i:Guguwa mai karfi ta lalata gidaje a jihar Kano

Date:

Guguwar iska mai ƙarfi ta yi barna a ƙaramar hukumar Bunkure da ke Jihar Kano, inda ta lalata gidaje da dama.

Daily Trust ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a ƙauyukan Sakafalle-Jalabi da Zangon Buhari, duk a yankin Kulluwa na ƙaramar hukumar, wanda ya bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Rufin gidaje da aka yi da ƙarfe (zinc) sun yi barna, haka kuma wasu gidajen da aka gina da tubalin kasa da siminti sun rushe sakamakon ƙarfin iskar da ta tashi a ranar Litinin.

Ko da yake ba a rasa rai ba, an yi asarar dukiyoyi masu yawa a yayin guguwar.

Fadan daba ya sa an hade Sallar Magariba da Isha’i a wata unguwa Kano

Jami’in yaɗa labarai na ƙaramar hukumar, Labaran Garba, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa babu wanda ya rasa ransa.

Wakilin Hakimin Bunkure, Nasiru Umar, ya kai rahoton lamarin a hukumance ga Sarkin Rano, Alhaji Isa Umar.

InShot 20250309 102403344

A yayin da yake bada umarnin a tattara cikakken rahoto game da lamarin domin mikawa majalisar ƙaramar hukuma don daukar matakin da ya dace, Sarkin ya shawarci mazauna ƙauyukan da abin ya shafa da su ɗauki matakan kariya daga irin waɗannan masifu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...