Ciyaman din Wudil ya ba da umarnin sassauta Totoci saboda rasuwar tsohon shugaban K/H

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban karamar hukumar Wudil Abba Muhammad Tukur ya ba da Umarnin sassauta duk tutocin dake fadin karamar hukumar don nuna alhini bisa rasuwar tsohon shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abubakar Abdullahi Likita.

” Mun ɗauki wannan matakin don Karrama aiyukan alkhairin da tsohon shugaban karamar hukumar ya yi na aiyukan raya kasa da Gina al’umma a fadin karamar hukumar Wudil”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran shugaban karamar hukumar Wudil Nura Mu’azu Wudil ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Da dumi-dumi: Yansanda a Kano sun kama yan daba 51 dauke da muggan makamai, tare da bayyana sunayensu

“Mun bayar da umarnin sassauta tutocin da ke cikin Sakatariyar karamar hukumar da duk wasu Hukumomi da cibiyoyin dake Wudil har na tsawon kwanaki uku (3) daga ranar Talata 17 ga watan Yuni 2025”.

Ya ce sun yi hakan ne a matsayin girmamawa da juyayi ga shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa wajen inganta ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, da hidima ga al’ummar Wudil.

InShot 20250309 102403344

Shugaban ya bukaci daukacin ma’aikata, mazauna yankin, da shugabannin al’umma da su hada kai wajen gudanar da addu’o’in nemawa marigayin rahamar Allah subhanahu wata’ala.

Hon. Abba Muhammad Tukur ya yi masa addu’ar Allah (SWT) ya gafarta masa ya sa ya na Aljannatul Firdausi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...