Ba Gaskiya a Labarin Rufe Kasuwar Singa Ranar Lahadi – Kwasangwami

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Shugaban kungiyar kwankwasiyya na kasuwar Singa Alhaji Liti Kwasangwami ya shawarci al’ummar kasuwar da su yi watsi da wata sanarwa da wata kungiya a kasuwar ta fitar na cewar yan kasuwar kar su fito domin yin kasuwancinsu ranar lahadi saboda sun shirya yin gangamin sharar kasuwar.

Alhaji Liti kwasamgwami ya sanar da haka ne a lokacin da ya ke zantawa da Kadaura24 a ofishinsa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Liti kwasamgwami ya ce wannan sanarwar da suka fitar bata da tushe ballantana makama, a don haka yake sanar da al’ummar kasuwar ta singa da su fito domin gudanar kasuwancinsu kamar yadda su ka saba a kodayaushe.

Neman suna ne ya sa Usman Alhaji ke sukar gwamnatin Abba Kabir Yusuf – kungiyar Nigeria Democracy Working Team

Shugaban kungiyar ya kuma yabawa Gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya yi kokari domin ganin Mahajjatan Kano sun gudanar da aikin hajjinsu lafiya.

Ya ce gwamnan jihar Kano injiniya Abba Kabir Yusuf ya taka mahimmiyar rawa ta fannin taimakawa alhazan jihar Kano da tallafin kudade da samar musu da ingantaccen matsuguni yayin gudanar da ibadarsu wanda kuma suka yi ta cikin kwanciyar hankali da lumana.

InShot 20250309 102403344

Shugaban kungiyar Alhaji kwasamgwami ya yi kira ga Gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf daya waiwayi kungiyar kwankwasiyya singa market bisa gudunmawar da take baiwa ci gaban gwamnatinsa musamma yadda wasu mutane su ke ganin kamar sun tura mota ta bulesu da hayaki.

Daga karshe shugaban kungiyar Alh liti kwasamgwami ya ce tunawa da kungiyar zai taimakawa kungiyar wajen fita daga cikin kalubalen yan adawa dake kokarin sare mata gwiwa da gatari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...