Abun da ya faru a Rano ba sai sake faruwa – Shugaban karamar hukumar ya tabbatar

Date:

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 

Shugaban karamar hukumar Rano malam muhd Naziru ya’u ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don ganin abun da ya faru a karamar hukumar bai sake faruwa ba.

” Tabbas mun yi takaicin abun da ya faru jiya ( Litinin) a karamar hukumar Rano, amma mun fara daukar matakan da suka dace domin ganin hakan ba ta sake faruwa ba a nan gaba”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Shugaban karamar hukumar ta Rano ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Kano.

Ya ce abubuwan da duka bangarorin guda biyu suka yi ba haka ya kamata ace sun yi ba, amma abun da ya faru ya riga ya faru kuma muna fatan hakan ba zai sake faruwa ba.

Sarkin Musulmi ya umarci yan Nigeria su fara duban watan Zulhijja

Malam Muhd Naziru ya yi kira ga al’ummar yankin musamman matasa da su guji daukar doka a hannu .Ya kuma bukaci al’ummar karamar hukumar da su kwantar da hankulansu komai yaci gaba da guda na ba tare da wata fargaba ba.

Ya ce yanzu haka tuni sauran Jami’an tsaro su ka dukufa domin ganin sun lalubo bata garin da suka kawo tashin hankali a karamar hukumar Rano.

InShot 20250309 102403344

Ya ce da zarar gwamna Abba kabir yusif ya dawo daga tafiyar da ya yi za su sanar da shi tare da ba shi cikakken rahoton musabbin mutuwar matashi Abdullahi musa da kuma na mutuwar babban baturen yan sandan karamar hukumar ta Rano.

ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalai da yan uwan Abdullahi Musa da na matashin da ya rasa ransa, haka zalika ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalai da kumar al’ummar jihar Nasarawa bisa rasuwar baturan yansanda na karamar hukumar Rano Baba Ali wanda Dan asalin jihar ta Nasarawa ne

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...