Rashin tsaro: Tinubu na ganawar sirri da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasa

Date:

A halin yanzu shugaba Bola Ahmed Tinubu ya na wata ganawar sirri da shugabannin hukumomin tsaro da kuma babban sufeton ƴansanda na kasa (IGP) a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

DAILY TRUST ta rawaito cewa wadanda su ka halarci ganawar sun hada da babban hafsan tsaron kasa, Janar Christopher Musa; Babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede; Hafsan Hafsoshin Sojan Sama, Air Marshal Hassan Abubakar; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla; da Sufeto Janar na ƴansanda, Kayode Egbetokun.

Ko da ya ke ba a fayyace cikakken bayanin taron ba har zuwa lokacin da Trust ta buga labarin, amma tattaunawar ba za ta rasa nasaba da sabbin hare-haren ƴan ta’adda a wasu sassan kasar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...