Barin jam’iyya bayan ka ci zabe a cikinta babban zunubi ne a Siyasa – Kwankwaso

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kano, sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya soki ƴan siyasar da ke sauya sheƙa bayan sun gama cin moriyar jam’iyyar, abin da ya bayyana da babban kuskure a siyasance.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a kwanakin baya ne dai wasu daga cikin yan majalisar wakilai da sanatan kano ta kudu suka fice daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanata Kwankwaso wanda ya bayyana hakan a Kano lokacin da yake karɓar wasu ƴan siyasar da suka sauya sheƙa zuwa NNPP daga ƙaramar hukumar Takai, a gidansa da ke Miller road a birnin Kano.

Gwamnatin da ta ke korar Ma’aikata ba ta Cancanci Wa’adi na biyu ba – Faizu Alfindiki

A baya-bayan nan ne dai raɗe-raɗi suka yi ta yawo cewa Kwankwason zai koma jam’iyya mai mulki ta APC.

Rabi’u Kwankwaso ya ƙara jaddada irin juriya da haɗin kai da ke tafiyar Kwankwasiyya duk kuwa da cewa an ta ƙoƙarin ganin an kawar da hankalin mabiya.

InShot 20250309 102403344

Ya ce dama kowanne zabe idan ya zo yana zuwa ne da darussan masu tarin yawa don haka ya ce Kwankwasiyya wani tsari ne da wani bai Isa ya wargaza shi ba, saboda tafiya ce ta akida ba ta kudi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...