Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Date:

Daga Shu’aibu Sani Bagwai

 

Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano ta bayar da kwangilar gina gada a garin Kwajale wadda za ta hada kauyuka bakwai har zuwa karamar hukumar Rimingado, akan kudi sama da Naira miliyan 160.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban karamar hukumar Alh. Bello Abdullahi Gadanya ya bayyana haka ne yayin kaddamar da aikin gadar a garin Kwajale.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya ce za a kammala aikin gadar ne cikin watanni biyu zuwa uku domin saukaka matsalar sufuri da jama’ar yankin ke fuskanta musamman a lokacin damina .

Gwamnatin Kano, za ta kula alakar Noma, kasuwanci da makamashi da kasar Morocco

Alh. Bello Gadanya ya bayyana cewa idan an kammala gadar gwamnan jihar Kano ya baiwa karamar hukumar tabbacin gudanar da aikin titin mai tsawon kilomita 15 da ya lalace wanda ya hada kauyuka bakwai daga Kiyawa har zuwa karamar hukumar Rimingado.

Shugaban ya yi kira ga al’ummar yankin da su cigaba da mara wa gwamnati baya saboda kokarin da gwamnatin jiha da ta karamar hukumar ke yi na bunkasa rayuwa da tattalin arzikinsu.

InShot 20250309 102403344

Dan kwangilar dake aikin Alh. Musa Ibrahim Badau, ya ce a matsayinsa na dan karamar hukumar ya bada tabbacin gudanar da aikin mai inganci kamar yadda aka yi yarjejeniya da shi.

Shi ma da yake nasa jawabin kansilan mazabar Rufa’i Isa ya yabawa shugaban karamar hukumar saboda gudanar da aikin gadar, inda ya ce sama da shekaru 10 suna bukatar a yi musu aikin amma ya gagara sai a wannan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...