Rikicin Siyasar Kano: Kashim Shattima ya ajiye Sako ga yan Siyasa

Date:

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya roki yan siyasar jihar Kano da su tuna irin zumuncin da ke tsakaninsu, inda ya rokesu da ka da su bari banbancin ra’ayin siyasa ya raba kansu.

Kashim Shettima ya yi wannan roko ne a gaban gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da Shugaban jam’iyar APC na jihar Kano Alhaji Abdullahi Abbas da sauran jiga jigan yan siyasa daga bangaren Kwankwasiyya da Gandujiyya a lokacin da ya ke ta’aziyar rasuwar Galadiman Kano marigayi Abbas Sunusi ranar Asabar da yamma.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kashim Shettima ya ce kuskure ne a jiha kamar kano da ake takama da ita a kowanne mataki na siyasa ta raba kan mutanan Kanon ko kawo cikas a a tsakaninsu.

“Jihar Kano itace abar koyi a duk Najeriya,dan haka bama murna idan munga ana samun sabanin ra’ayin siyasa kuma ana nunawa juna yatsa,” acewar Shettima

Yace Kano itace cibiyar Arewa ,duk abinda ya shafi Kano ya shafi Arewa.

Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya rage farashin man fetur a Nigeria

“Wannan tasa na ke fadar wannan sako da harshen Hausa,duk dacewa ni ba cikakken bahaushe bane ,amma na kokarta na fada muku wannan sako da hausa ne domin ku fahimta sosai,”Inji Kashim Shettima

Yayi fatan Allah yaji kan marigayi Galadiman Kano yasa yana Aljanna.

InShot 20250309 102403344

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma jajantawa iyalan wadanda akayi garkuwa da dan uwansu a karamar hukumar Shanono da wadanda suka rasa rayukansu lokacin harin da yan bindiga suka kai yankin.

“Muna rokon Allah ya bamu zaman lafiya a Najeriya da kasa baki daya,”Inji Kashim.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...