Gwamnatin Nigeria za ta ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Majalisar Zartarwa ta Najeriya ta amince da ci gaba da sayar da danyen mai a cikin gida da kudin Naira, cikin wani mataki da ta ce zai taimaka wajen inganta tattalin arzikin kasar.

Ma’aikatar Kuɗi ta bayyana hakan ne a shafinta na X, inda ta ce wannan ba mataki ne na wucin-gadi ba, sai dai tsari ne da ake son ya ɗore wanda Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, ta aminta da shi.

InShot 20250309 102403344

Wannan shawara ta zo ne bayan tattaunawa tsakanin manyan jami’an gwamnati da kuma masu ruwa da tsaki a fannin man fetur a zaman majalisar na wannan mako.

Ana hasashen wannan tsarin zai inganta harkokin kasuwancin man fetur a cikin gida, tare da rage dogaro da kasashen waje wajen siyo danyen mai.

Shawarar ta samu goyon bayan manyan ministoci a taron Majalisar Zartarwa, wanda ya kara bayyana kudurin gwamnatin Najeriya na inganta tsaro da kuma bunkasa masana’antar mai.

Yanzu-yanzu: Sarki Sanusi ya nada sabon Galadiman Kano

A ranar Talata ne manyan jami’an Ma’aikatar Kuɗi, NNPCL, FIRS, CBN, da wasu manyan hukumomi suka gana domin duba yadda aikin ke tafiya da kuma magance matsalolin da ka iya tasowa a tsawon lokacin aiwatar da shirin.

“Mun fahimci cewa sauye-sauye irin wannan suna zuwa da ƙalubale,” in ji wani jami’i daga cikin mahalarta taron.

“Amma dukkanin hukumomin da ke da hannu a cikin shirin sun ƙudiri aniyar ganin an cimma nasara.”

A baya-bayan nan NNPCL ya daina sayar wa matatar Dangote ɗanyen mai a farashin Naira bayan ƙarewar yarjejeniyar da suka ƙulla.

Hakan ya haifar da tashin farashin man fetur a gidajen mai a faɗin ƙasar nan, lamarin da masana suka ce hakan zai sake shafar tattalin arziƙin Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...