Saudiya ta sanar da ranar da masu aikin Umrah za su bar kasar

Date:

Ma’aikatar aikin Hajj da Umrah ta Saudi Arabiya ta kebe ranar 1 ga watan Dhul Qada, wadda ta zo dai-dai da 29 ga watan Afrilu, a matsayin ranar karshe da duk wani bako da ya shiga kasar domin yin Umrah ya fice.

Ma’aikatar ta ce ta dauki matakin ne domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa.

InShot 20250309 102403344
Talla

Cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta ce ranar 15 ga watan Shawwal, da ya yi dai-dai da 13 ga watan Afrilu, ita ce ranar karshe da masu shiga kasar domin aikin Umrah za su daina shiga, sai dai a fita.

Ma’aikatar ta jaddada cewa duk wanda aka samu ya ci gaba da zama a kasar har ya wuce lokacin da kebe, to ko shakka babu ya saba ka’ida sannan kuma zai fuskanci hukunci.

Mun gamsu da yadda malamai da daliban su ka koma makarantu – Gwamnatin Kano

Daga nan ta bukaci mutane da ma kamfanonin da ke shirya zuwa aikin Umrah da su kiyaye da wadannan lokuta da aka kayyade.

Ma’aikatar ta yi gargadin cewa duk wani jinkiri na barin mutane kasar za a dauke shi kamar karya doka.

Ta ce duk kamfanin da aka samu da kin bayyana mutanen da suka ki koma wa kasashensu to za a ci tararsu riyar dubu 100.

Daily Nigerian

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...