Shugaban K/H Dala ya kaddamar da aikin hanya na kusan Naira miliyan 200 a mazabar Gobirawa

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo Ibrahim Imam ya kaddamar da aikin hanya da za’a kashe sama da Naira miliyan 197 a yankin Gobirawa Daiba dake karamar hukumar.

Da yake Kaddamar da Aikin Shugaban Karamar Hukumar ya bukaci dan kwangilar da zai yi aikin da ya yi aiki mai inganci da nagarta Sannan ya sanya matasan yankin a cikin wadanda za su yi Aikin a wasu bangarorin Aikin.

InShot 20250309 102403344
Talla

“Mun ware wadannan kudaden ne domin gudanar da aikin Wannan hanya mai matukar muhimmancin gaske ga al’ummar, kuma Muna da yakinin idan an kammala aikin al’ummar wannnan yankin da makwaftansu za su ji dadin aikin, domin zai taimaka wajen rage musu wahalhalun da suke fuskanta a yanzu da kuma bunkasa tattalin arzikinsu”. Inji Suraj Imam

Alhaji Surajo Imam ya kuma ce kamfanin Nomora Integrated service ne aka Baiwa kwangilar aikin kuma an Riga an biyasu kaso hamsin cikin dari na kudin Aikin.

Rundunar Yansanda ta ba da sabon umarni kan gayyatar da ta yi wa Sarki Sanusi

Ya yi kira ga al’ummar yankin da su baiwa dan kwangilar hadin kan da ya dace domin samun nasarar kammala aikin akan lokaci.

Suma wasu mazauna Yankin Alhaji Mustapha Abdulmajid A.Z da Naziru Gambo sun bayyana farin cikin Su bisa Samun wannan Aikin suna Masu cewar Aikin hanyar ya Dade Yana ci musu tuwo a kwarya

A karshe Cikin wata Sanarwa da Jami’ar Hulda da Jama’a ta Karamar Hukumar Dala Hassana Aminu ta sanyawa hannu tace wakilin kamfanin da zaiyi Aikin Alhaji Tasiu yayi Alkawari zasuyi Aikin Mai inganci da nagarta Kuma zasuyi Shi akan Lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...