Tinubu Atiku da Kwankwaso sun bayyana kaduwarsu da rasuwar Sheikh Dutsen Tanshi

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya baiyana kaduwar sa da rasuwar malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi.

Dutsen Tanshi ya rasu ne a juya Alhamis da daddare a garin Bauchi, inda a safiyar yau Juma’a aka yi jana’izar sa.

A wata sanarwa da Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ya fitar a yau Juma’a, Tinubu ya ce rasuwar Dutsen Tanshi doke ta girgiza al’umma duba da yadda ya dora miliyoyin matasa akan hanyar addinin Islama.

InShot 20250309 102403344
Talla

Tinubu ya kuma yabawa ƙoƙarin marigayin wajen adawa da tsaurin ra’ayin addini da ƴan Boko Haram ke yi, musamman a farkon fitowar su.

A karshe Tinubu ya taya iyali da al’ummar jihar Bauchi da ma kasa baki daya alhinin rasuwar, inda ya yi addu’ar Allah Ya gafarta masa, Ya kuma badq haƙurin rashin sa.

Tinubu ya kuma horo matasa ɗaliban ilimi da su yi koyi da irin rayuwar ilimi da marigayin ya yi.

Dambarwar Rivers: AIG Gumel ya gamu da fushin Sufeto Janar na yan sandan Nigeria

Haka shi ma tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya ce ya kadu sosai da samun labarin malamin, inda ya bayyana shi a matsayin jigo wajen yada addinin musulunci.

Tsohon gwamnan jihar Kano Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso ma ya bayyana rasuwar Sheikh Dutsen Tanshi a matsayin babban rashi ga al’ummar Musulmi baki daya.

Dukkaninsu sun yi wa malamin fatan samun Rahamar Allah subhanahu wata’ala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...