Ku zama nagari masu juriya don cimma burikanku – Waiya ya fadawa Matasan Kano

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya yi kira ga matasa da su guji son zuciya da gaggawar neman cimma burikansu ta kowacce hanya.

Kwamishinan ya yi kiran ne a lokacin da ya gana da wata tawaga ta ƙungiyar F10 Initiative da ta ziyarce shi a ofishinsa.

InShot 20250309 102403344
Talla

Cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa-hannun SDaraktan ayyuka na Musamman na ma’aikatar yaɗa labarai, Sani Abba Yola ya ce Kwamishinan ya ce matasa su riƙa haƙuri da biyayya, tare da wadatuwa da abin da Allah ya ba su. Ya kuma nuna cewa duk wani ci gaba na rayuwa yana buƙatar juriya da sadaukar da kai.

A cewar Waiya, matasa su ne ginshikin al’umma, saboda haka gwamnati za ta ci gaba da tallafa musu. Ya kuma yaba wa ƙungiyar F10 Initiative saboda ayyukanta na inganta rayuwar al’umma.

Gwamnan Kano ya bayyana dalilin da yasa ya sake dawo da Sarkin Gaya

Daga ɓangarensu, Daraktan ƙungiyar F10 Initiative, Abbas Abdullahi Yakasai, ya ce ƙungiyarsu ta ƙunshi ƙungiyoyi 50, waɗanda suka haɗu don ba da fifiko ga ci gaban Jihar Kano.

Ya kuma yaba wa Kwamishinan saboda rawar da yake takawa wajen inganta harkokin yada labarai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...