Dr. Hakeem Baba-Ahmed, mai ba Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara kan harkokin siyasa, ya yi murabus, kamar yadda jaridar Daily Trust ta samu labari daga ingantattun majiyoyi.
Majiyoyi daga fadar shugaban kasa sun tabbatar jiya cewa tsohon kakakin kungiyar dattawan Arewa (NEF) ya mika takardar murabus dinsa kusan makonni biyu da suka gabata.

Daily Trust ta rawaito cewa majiyoyin sun ce Dr. Baba-Ahmed bai bayyana dalilan murabus din na sa ba, sai dai kawai ya ce yana da nasaba da dalilai na kashin kansa.
Duk da haka, a lokacin hada wannan rahoto, ba a tabbatar ko fadar shugaban kasa ta amince da murabus dinsa ba, in ji Daily Trust.
An nada Baba-Ahmed a matsayin Mai Ba da Shawara na Musamman kan Harkokin Siyasa a Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima a watan Satumba na 2023.
Gwamnan Kano ya bayyana dalilin da yasa ya sake dawo da Sarkin Gaya
A cikin watanni 17 da suka gabata, ya wakilci fadar shugaban kasa a taruka daban-daban na jama’a, ciki har da wani taron kasa da aka shirya mai taken: “Karfafawa Dimokuradiyyar Najeriya: Hanyar Kyakkyawan Mulki da Ingancin Siyasa,” wanda aka gudanar daga 28 zuwa 29 ga Janairu, 2025, a Abuja.